Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta MDD tace ana fargabar daruruwan ‘yan gudun hijira ne suka halaka, ko ba’a San inda suke ba, sakamakon nutsewar wasu jirage a tekun Meditarrenean, a cikin kwanaki 10 da suka wuce dalilin mummunar yanayi cikin teku, kamar yadda hukumar ta fada ranar Litinin.
“Sai dai tayiwu adadin wadanda suka halaka ya haura haka, wadda yake kara nuni da cewa wannan hanyar itace mafi hadari a duk fadin duniya da ‘yan gudun hijira suke bi, inji hukumar ta MDD.
Yara tagwaye ‘yan mata biyu suna daga cikin wadanda aka tabbatar da mutuwar su a Lampedusa a Italiya, bayan wani kokarin ceto kan wani jirgin ruwa da ya taso daga Tunisia. Sanyi ne ya kashe ‘yaran tare da wani mutum, kamar yadda uwar ‘yaran daga kasar Guinea wacce ta tsira, ta fada, inji hukumar ta MDD.


