Hukumomin Jami’ar tarayya ta Kashere da ke jihar Gombe sun karyata rahotannin kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ‘yan bindiga sun kai hari jami’ar, inda ta bayyana labarin a matsayin ƙarya.
A cikin wata sanarwa da jami’ar yada labarai, Janet Ezekiel, ta sanya wa hannu, jami’ar ta ce babu wani hari da ya faru, kuma an ƙirƙiri labarin ne domin tayar da hankalin ɗalibai da kawo cikas ga jarabawar zangon farko.
Jami’ar ta bayyana cewa abin da ya faru a yankin rikici ne tsakanin matasan ƙauyukan Jauro Buba da Garin Rigiya, ba tare da alaƙa da jami’ar ba, ta ƙara da cewa kuma hukumomin tsaro sun shawo kan lamarin.
Shugabancin jami’ar ya tabbatar wa ɗalibai da iyaye cewa harabar jami’ar na cikin kwanciyar hankali, tare da kira ga jama’a da su dogara ga sahihan hanyoyin sadarwar jami’ar kawai.


