Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Haɗin Gwiwar GOSERC Da Savannah Zai Ƙarfafa Rarraba Wutar Lantarki A Faɗin Jihar Gombe
Published: July 29, 2026 at 10:55 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta jihar Gombe (GOSERC) ta gudanar da wani muhimmin taro da mahukuntan Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Savannah, a wani mataki na ƙarfafa haɗin gwiwa domin inganta rabon wutar lantarki a faɗin Jihar Gombe.

Da yake zantawa da Manema labarai bayan kammala taron, Shugaban Hukumar, Dakta Usman Abba Arabi, ya bayyana cewa manufar taron ita ce samar da dabarun haɗin gwiwa da za su tabbatar da inganta samar da wutar lantarki ga al’ummomin jihar.

Ya ce Gwamnatin jihar Gombe ce ta kafa Hukumar GOSERC domin tsara da kuma sa ido kan harkokin kasuwar wutar lantarki a yankunan karkara da birane, tare da tabbatar da cewa masu amfani da wutar lantarki sun samu ingantaccen sabis.

Dakta Usman Abba Arabi ya jaddada cewa Hukumar za ta ci gaba da aiwatar da ayyukanta yadda ya kamata, yana mai bayyana fatan cewa nan ba da jimawa ba al’ummar jihar za su fara cin gajiyar ingantacciyar, tabbatacciya kuma mai sauƙin samu ta fuskar farashi.

A nasa jawabin, Jagoran Tawagar Kamfanin Savannah Electricity Distribution Company, Abiddeen Olariwaju, ya bayyana cewa kamfanin sabon reshe ne na Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Jos (JED), wanda aka kafa bayan fara aiki da Dokar Wutar Lantarki ta shekarar 2023, wadda ta bai wa jihohi damar tsara da gudanar da kasuwar wutar lantarki a yankunansu.

Olariwaju ya ce kamfanin ya tanadi tsare-tsare na gajeren lokaci, matsakaicin lokaci da kuma na dogon lokaci domin bunƙasa samar da wutar lantarki a Jihar Gombe.

Ya ƙara da cewa an riga an fara gyaran na’urorin rarraba wutar lantarki (transformers) a garin Bajoga, hedikwatar Ƙaramar Hukumar Funakaye, da kuma wasu sassa na cikin birnin Gombe, a matsayin matakin farko na aiwatar da shirin.

Ya tabbatar da cewa kamfanin zai ci gaba da aiki tare da Hukumar GOSERC da sauran masu ruwa da tsaki domin tabbatar da samar da ingantacciyar wutar lantarki ga daukacin al’ummar jihar Gombe.

Har ila yau, Olariwaju ya yaba wa Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa rattaba hannu kan Dokar Wutar Lantarki ta jihar Gombe, yana mai cewa hakan ya sanya Gombe cikin jihohi goma na farko a Najeriya da suka kafa cikakkiyar hukuma mai kula da harkokin wutar lantarki a matakin jiha.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sana'o'i, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Kwamitin Ardo Chindo Ya Buƙaci A Hana Mamaye Filayen Kiwo da Gandun Daji
Next Post: Tinubu Ya Kawo Ƙarshen Aikin Kwamitin Sayar Da Kaddarorin Gwamnati

Karin Labarai Masu Alaka

Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja Afrika
Rasha Ta Gargadi Amurka Da Isra’ila Kan Harin Iran Afrika
Harin Isra’ila A Gaza Da Jirgi Maras Matuki Ya Kashe Mutane Afrika
An Samu Bullar Cutar COVID 19 A Najeriya Afrika
Ƙungiyar Mata Sunyi Kira Ga Jam’iyar P R P Da Ta Dauki Baheejja A Matsayin Mataimakiyar Gwamnan A Bauchi 2027 Labarai
Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutun Sallar Azumi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya Amurka
  • Sakataren Kungiyar NATO Yayi Magana Da Hukumomin Kasashe Afrika
  • Kasar Saudiya Zatayi Gwajin Noman Dabino A Kano Labarai
  • Kwamitin Aikin Hajjin Najeriya Ya Shigar Da Korafi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Yankewa Prime Ministan Kasar Tunisiya Hukuncin Shekaru 24 A Gidan Yari Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya kori Wasu Hadimansa Bisa Cin Zarafin Kansila Najeriya
  • Kasar Togo Ta Kori Paul Henri Damiba Zuwa Kasar Sa Ta Haihuwa Afrika
  • Turkiyya Tana Gudanar Da Binciken Kasar Da Suka Kona Tutar Ta Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.