Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano
Published: December 1, 2025 at 4:00 PM | By: Mahmud Kwari | Updated: December 1, 2025

Hukumar kare hakkin dan Adam ta Najeriya tace kawancen aiki data kulla da Kotun Sulhu ta jihar Kano (Kano Multi-Door Court) yana haifar da sakamako mai kyau, ta fuskar warware matsalolin danne hakkoki a tsakanin al’uma.

A taron kaddamar da sabbin mambobin majalisar kula da ayyukan Kotun, shugaban Ofishin shiyyar Kano na hukumar Abdullahi Shehu yace, aiki kafa da kafa da Kotun Sulhun ta Kano na taimakawa bangaren sasanta Jama’a da sulhunta su na hukumar, inda a cewar sa, hadin gwiwar ke bada dama su dai-daita mutanen dake takaddama da juna cikin karamin lokaci.

An kafa Kotun Sulhu ta Kano ne tun kimanin shekaru 20 da suka shude, domin sasanta mutanen dake takaddama da juna akan al’amura daban daban, a wani mataki na rage cunkoson kararraki a gaban kotuna da-ma gidajen yari.

Kotun mai hurumin hukunci dai-dai dana babbar kotun jiha (State High Court), na sauraron kararraki ko korafe-korafe da suka shafi Cinikayya, takaddamar Aure, hakkin makwaftaka da sauran batutuwan yau da kullum na rayuwar Jama’a.

Kotun na aiki tare da hukumomin tsaro, musamman hukumar ‘yan sanda da kungiyoyin kare hakkin bil’adama, Malaman addini, shugabanni al’uma da masu rike da sarautu.

Babbar Jojin Kano, mai shari’a Dije Aboki, ta bukaci Jama’a su kara kaimi wajen amfani da damammakin da Koton ke bayarwa na saukaka shari’u da kuma fito da hakki babu bata lokaci.

Cunkoson kararraki a gaban alkalai a Najeriya na cikin manyan kalubalen da ‘yan kasar ke fuskanta wajen samun adalci a kotuna, musamman wadanda ke tsare a gidajen yari na suna dakon a yanke musu hukunci.

 

Labarai

Post navigation

Previous Post: Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi
Next Post: Nada Jakadu Da Tinubu Yayi Sako Ne Ga ‘Yan-Arewa

Karin Labarai Masu Alaka

Shugabannin Sojojin Najeriya sun Kai Ziyarar Aiki Maiduguri  Afrika
Ministan Harkokin Wajen Iran Yagana Da Shugaban Sa’ido Akan Nukiliya Afrika
‘Yan Tawayen Kasar Kwango Ne Suka Kai Hari Filin Jirgin Saman Kisangani Labarai
Sakamakon Yakin Gabas Ta Tsakiya Kowacce Gangar Mai Ta Haura Dala 100 Afrika
Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri Afrika
Kasar Malawi Ta Kaddamar Da Rigakafin Shan Inna Kiwon Lafiya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kyautata Dangantaka Tsakanin Jami’an Tsaro Da Al’umma Ce Mafita Najeriya
  • Shugaban Kasar Iran Yace Kasar Bata Da Kiyayya Tsakaninta Da Amurkawa Afrika
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Asabar 11.15.2025 Rediyo
  • Majalisar Tattalin Arzikin Najeriya Ta Bawa Gwamnan Kebbi Mukamin Kyautata Harkar Kiwo Najeriya
  • Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Fadar Sarkin Musulmi: Talata Ne 1 Ga Watan Sha’aban Na 1447AH Najeriya
  • Tinubu Yafara Wasu Dabaru Domin Samun Kuri’u Siyasa
  • Yau Lahadi Ake Gudanar Da Zabe A Kasar Myanmar Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.