CP Chuso Ya Yaba da Matakan Gwamnatin Gombe Wajen Rage Rikicin Makiyaya Da Manoma
Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, ya ce ci gaba da tattaunawa da kuma daukar matakin gaggawa kan matsalolin da ke tasowa shi ne mafita wajen hana rikice-rikicen makiyaya da manoma a jihar. CP Chuso ya bayyana haka ne yayin taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki kan rikicin makiyaya da manoma…

