Wata Kotu A Abuja Ta Wanke Abba Kyari
Babbar kotun tarayya da ke Abuja a Najeriya ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a James Omotosho ta wanke tare da sallamar dakataccen mataimakin kwamishinan ‘yan sanda Abba Kyari daga tuhume-tuhume guda 23 na zargin kin bayyana kadarori kamar yadda gidan talabijin na TVC ya rawaito. Hukumar NDLEA ce ta shigar da karar, inda ta tuhumi Kyari tare…

