Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Iran Da Amurka Zasu Kulla Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
  • Channels TV: Ta Yi Rashin Hazikin Dan Jarida Mr Khani Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika
  • Anyi Sallar Rokon Ruwa A Saudiya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka

Dan Ra’ayin Mazan Jiya Leo Brent Zai Kyautata Alakar Afirka Ta Kudu Da Amurka
Published: February 17, 2026 at 9:49 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mutumin da shugaban Amurka Donald Trump ya nada jakadan kasar a Afirka ta kudu, dan gwagwarmaya mai ra’ayin mazan jiya Leo Brent Bozell na uku, wanda kuma marubuci ne ya sauka kasar, inda zaiyi aiki domin gyara dangantaka tsakanin kasashen biyu wanda yayi tsami.

Wani jami’i a ofishin jakadancin Amurka ya fadawa kamfanin dilancin labarai na Reuters cewa, Ambasda Bozell ya iso. Kuma ana sa ran zai gabatarwa shugaba Cyril Ramaphosa takardunsa gabannin ya fara aiki.

Dangantaka tsakanin hukumomi a Washington da Pretoria sunyi baya ainun bara, yayinda Trump yake sukar kasar cewa tana muzgunawa tsiraru farar fata, ya soki mu’amalar kasar da Rasha da kuma China, sannan ya aza mata haraji mai yawa kan kayayyaki daga kasar.

Afirka ta kudu bada ta da jakada a Washington tun cikin watan Yunin bara, bayanda shugaba Trump ya kori jakadan Afirka ta kudu Ibrahim Rasool, daga kasar.

A lokacin da ake tantance shi cikin watan Oktoban bara, Ambasada Bozell yace zai tunkari aikinsa tare da girmamawa ga al’umar Afirka ta kudu, kuma yana ganin akwai damar kulla dangantaka mai dorewa duk da cewa akwai sassan da suke da sabanin ra’ayi.

Afrika, Amurka

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Tawaye A Burkina Faso Sun Kashe ‘Yan Kasar Ghana
Next Post: Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Shugaban Makaman Nukiliya

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar ISIS Ta Dauki Alhakin Harin Kasar Nijar Afrika
Babu Dabbar Da Zata Sake Shiga Amurka Daga Mexico! Amurka
Ghana Tayi Watsi Da Yarjejeniya Akan Hakar Ma’adanai Afrika
Jagoran Kasar Iran Yace Basa Bukatar Tallafin Kasar Amurka Afrika
‘Yan Kasar Venuzuela Zasu Fara Komawa Gida Amurka
Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Dottin Shara Ya Damu Jama’ar Havana Kasar Cuba
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Shugaban Makaman Nukiliya
  • Dan Ra’ayin Mazan Jiya Leo Brent Zai Kyautata Alakar Afirka Ta Kudu Da Amurka
  • ‘Yan Tawaye A Burkina Faso Sun Kashe ‘Yan Kasar Ghana
  • Dakarun Sojin Amurka Sunfara Sauka A Najeriya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutu Najeriya
  • Kirana Ga ‘Yan Siyasar Arewa, Su Jira Sai 2031- Akume Labarai
  • Jakadan Kasar Sin a Najeriya Ya Ziyarci Tinubu Najeriya
  • Shugaban Guinea-Bissau Umaro Na Fuskantar Matsin Lamba Afrika
  • An Hana Yada Rahotannin Siyasa A Kasar Uganda Tsaro
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Iran Ta Kama Wani Jirgin Ruwa Shake Da Mai Labarai
  • Tattalin Arzikin Kasar Botswana Zai Farfado Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.